Episodios

  • Wa Zai Gaji Buhari A Fagen Siyasar Najeriya?
    Jul 15 2025

    Send us a text

    Gaskiya da rikon amana suna cikin dalilan da suka sa tsoon Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi fice a siyasar Arewacin Najeriay.

    Wasu masana da ma makusantar tsohon Shugaban kasar dai suna ganin Arewa ta yi rashi kuma zai yi wuya a samu makwafansa.

    Yayin da ake binne marigayin, hankalin wasu 'yan Najeriya ya fara komawa ga yiwuwar samun wanda zai iya maye gurbinsa a fagen siyasar Najeriya.

    wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

    Más Menos
    24 m
  • Abin Koyi Daga Rayuwar Marigayi Muhammadu Buhari-- Makusantansa
    Jul 14 2025

    Send us a text

    Rasuwar tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ta sa 'yan Najeriya da dama kaduwa duk da cewa ya jima yana fama da rashin lafiya.


    Sanar da rasuwar ke da wuya, 'yan kasa suka fara bayyana ra'ayoyi daban daban akan abin da suka gani game da rayuwar tsohon shugaban.

    Amma makusantansa sun bayyana wasu halaye game da shi wadanda ba kowa ne ya sani ba.


    Sune kuma shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

    Más Menos
    25 m
  • Dalilan Da Wasu Matasa Ba Sa Aiki Tukuru Wajen Neman Arziki
    Jul 11 2025

    Send us a text

    Matasan Najeriya da dama suna son yin arziki amma ba tare da sun sha wahala ba.


    Sau da yawa matasa sun fi neman hanya mafi sauki da za ta basu arziki ba tare da sun sha wahala ba.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa wasu matasa bin yanke don tara abin duniya.

    Más Menos
    25 m
  • Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata
    Jul 10 2025

    Send us a text

    Duk da amfanin kifi ga lafiyar jikin mutum da kuma samar da kudin shiga masana sun ce ba a amfani da shi yadda ya kamata a Najeriya.


    Baya ga bai wa jiki lafiya, kifi ka iya samar da kudaden shiga ga daidaikun ’yan Najeriya da ma kasar gaba daya.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa ’yan Najeriya basa samun cin kifi kamar yadda ya kamata.

    Más Menos
    28 m
  • Sarkakiyar Dake Gaban Hadakar ADC -- Atiku Ko Peter Obi?
    Jul 8 2025

    Send us a text

    'Yan Najeriya suna ci gaba da tafka muhawara a kan wanda jamiyyar hadaka ta ADC zata tsayar takarar Shugaban Kasa a zaben 2027.


    Yayin da wasu suke ganin Atiku Abubakar yana da dimbin magoya baya, wasu kuwa gani suke yi shi ma Peter Obi ba kanwar lasa bane.

    Ko me zai faru idan daya daga cikin su ya samu tikitin tsayawa takara a 2027?


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan wannan lamari.

    Más Menos
    27 m
  • Mene Ne Tasirin Nadin Mataimaka Na Musamman A Rayuwar Jama’a?
    Jul 7 2025

    Send us a text

    Wadanda aka zaba su rike mukaman gwamnati kan nada wasu mukarrabai don su taya su sauke nauyin da aka dora musu.


    Wasu na zargin nadin baya rasa nasaba da sakayya ga irin rawar ga wadanda aka nada saboda rawar da suka taka yayin yakin neman zabe.

    Ko irin wadannan nade-nade na da wani tasiri ga rayuwar alumma?


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan nade-naden masu taimakawa shugabanni da irin tasirin da suke dashi.

    Más Menos
    26 m
  • Shin Ko Hadakar Sabuwar Jamiyyar ADC Za Ta Fidda Wa ‘Yan Najeriya Kitse Daga Wuta?
    Jul 4 2025

    Send us a text

    Yan Najeriya da dama na ta bayyana mabanbantan ra’ayoyi kan sabon hadakar ‘yan siyasa zuwa sabuwar jami’yyar ADC.


    A yayin da wasu ke ganin wannan hadaka za ta cire musu kitse daga wuta, wasu kuwa gani suke yi duk kanwar ja ce.

    A ranar laraban nan ne dai gaggan ‘yan siyasa daga jamiyyu daban daban suka hadu don dinkewa wuri daya da niyyar kalubalantar jamiyya mai mulki ta APC, a cewar su za su ceto Najeriya daga halin da jamiyyar ta jefa su a ciki.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan ko sabuwar hadakar jamiyyar ADC za ta fidda ‘yan Najeriya daga matsalar da suka ce suna ciki?

    Más Menos
    27 m
  • Boyayyun Kalubalen Da Sabuwar Hadakar ADC Za Ta Iya Fuskanta
    Jul 3 2025

    Send us a text

    Tun kafin sanar da sabuwar kawance da suka hada da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da Peter Obi da Nasir El’rufai da wasu manyan ‘yan siyasa ne aka fara zargin yiwa wannan hadaka zagon kasa da kawo cikas ga tafiyar wannan hadaka.


    Daya daga cikin irin wadannan zagon kasa da ake zargin wasu da yiwa wannan sabuwar hadaka itace na sanar dasu rashin samun dakin taron da suka shirya gudanar da taron lokaci kalilan gabanin taron.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan boyayyun kalubalen da sabon hadakar jamiyyar ADC zata iya fuskanta gabanin 2027.

    Más Menos
    28 m