Najeriya a Yau Podcast Por Muslim Muhammad Yusuf Ummu Salmah Ibrahim arte de portada

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau

De: Muslim Muhammad Yusuf Ummu Salmah Ibrahim
Escúchala gratis

OFERTA POR TIEMPO LIMITADO. Obtén 3 meses por US$0.99 al mes. Obtén esta oferta.

Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.

© 2025 Najeriya a Yau
Ciencia Política Política y Gobierno
Episodios
  • ‘Halin Kunci Ya Sa Muke Zama A Baca A Abuja’
    Oct 6 2025

    Send us a text

    Halin matsin tattalin arziki ya tilasta da yawa daga cikin mutane zama a bacoci a garin Abuja da wasu biranen Najeriya.


    Mutane a birane kamar Abuja da Legas Da Fatakwal na cikin halin matsi sakamakon rashin ingattaccen muhalli.

    Ko wannen irin rayuwa irin wadannan mutanen ke yi?


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai a yau da ake bikin ranar muhalli ta duniya.

    Más Menos
    27 m
  • Yadda Fasahar AI Ke Barazana Ga Sana’ar Masu Shagunan Daukar Hoto
    Oct 3 2025

    Send us a text

    A zamanin yau na fasahar zamani, musamman fasahar kirkirarriyar basir ta (AI), harkokin sana’o’i da dama suna fuskantar sauye-sauye masu girma. Daya daga cikin sana’o’in da ke cikin babban hadari shi ne sana’ar ɗaukar hoto musamman irin wadanda ke kashe makudan kudi wajen sayen kyamara da bude katafaren gidajen daukar hoto.


    A da, mutane kan je shagon daukar hoto domin samun hoto mai kyau na fasfo ko na bikin aure ko bikin suna, ko kuma kowane irin taron biki. Amma yanzu, manhajojin AI suna ba wa mutane damar kirkirar irin wadannan hotuna daga wayoyin su ko kwamfuta cikin mintuna kadan ba tare da zuwa shagon daukar hoto ba.

    Wannan yanayi na iya jefa masu shagunan daukar hoto cikin matsala ta rashin samun kudin shiga da kuma rasa sana’ar gaba ɗaya, muddin ba su bullo da sabbin dabarun jawo hankalin kwastomomi ba.


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba akai.

    Más Menos
    23 m
  • Abin Da Dokar Kasa Ta Ce Kan Takarar Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan
    Oct 2 2025

    Send us a text

    Batun siyasar Najeriya ya sake ɗaukar hankali yayin da jam’iyyar PDP ta bayyana cewa tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Ebele Jonathan, zai tsaya mata takarar shugaban ƙasa a 2027.
    Wannan batu ya tayar da muhawara mai zafi a tsakanin masana, da ‘yan siyasa da ma al’umma.


    Idan za a iya tunawa dai, an rantsar da tsohon shugaban ƙasan, har sau biyu: a karo na farko a shekarar 2010 bayan rasuwar tsohon shugaban kasa Umaru Musa Yar’adua, sannan kuma a karo na biyu a 2011 bayan lashe zaben da ya biyo baya.

    Amma abun tambayar a nan shine, shin ko me dokar kasa ta bayyana kan takarar tsohon shugaban kasan bayan rantsar dashi har sau biyu kan karagar mulki?
    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.


    wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

    Más Menos
    27 m
Todavía no hay opiniones