Najeriya a Yau Podcast Por Muslim Muhammad Yusuf Ummu Salmah Ibrahim arte de portada

Najeriya a Yau

Najeriya a Yau

De: Muslim Muhammad Yusuf Ummu Salmah Ibrahim
Escúchala gratis

Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.

© 2025 Najeriya a Yau
Ciencia Política Política y Gobierno
Episodios
  • Yadda Takunkumin Amurka Zai Shafi Tattalin Arzikin ‘Yan Najeriya
    Dec 18 2025

    Send us a text

    Takunkumin da Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya sanya wa wasu ‘yan Najeriya ya sake jawo hankali kan irin tasirin manufofin ƙasashen waje ga rayuwar mutane da tattalin arzikin ƙasa baki ɗaya.


    Wannan takunkumi, wanda ya haɗa da hana shiga Amurka, da toshe kadarori ko hana mu’amala da wasu hukumomi da kamfanonin Amurka, ba wai hukunci ne ga mutum ɗaya kaɗai ba, kazalika yana da tasiri mai zurfi ga harkokin kasuwanci, zuba jari da martabar ƙasa a idon duniya.

    Ko ta yaya wannan takunkumi zai shafi tattalin arzikin daidaikun wadanda abun ya shafa, da ‘yan uwansu da ma Najeriya baki daya?


    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

    Más Menos
    16 m
  • Ce-ce Ku-ce Da Ya Dabaibaye Dauke Shalkwatar Bankin Masana’antu Zuwa Legas
    Dec 16 2025

    Send us a text

    Batun matakin da gwamnatin tarayya ta dauka na mayar da shalkwatar Bankin Masana’antu zuwa jihar Legas ya haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin ’yan Najeriya. Wannan mataki ya tayar da mabanbantan ra’ayoyi daga bangarori daban-daban na al’umma, inda wasu ke kallonsa a matsayin shawara mai ma’ana da za ta karfafa harkokin masana’antu da jawo jarin cikin gida da na kasashen waje.


    Sai dai a daya bangaren kuma, akwai masu sukar wannan mataki, inda suma suka bayyana irin tasu damuwa kan batun.


    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan wadannan takaddama da kuma abun da kowanne gefe ke bayyanawa.

    Más Menos
    15 m
  • Matakan Da Jami’an Tsaro Ke Dauka Kan Tafiye-tafiyen Kirsimeti
    Dec 15 2025

    Send us a text

    A ’yan shekarun nan, lokaci na bukukuwan ƙarshen shekara—wanda a da ake ɗauka a matsayin lokacin farin ciki, da haɗuwa da iyalai, da tafiye-tafiye—ya fara sauya salo ga mutane da dama. Maimakon shirye-shiryen ziyartar ’yan uwa ko halartar bukukuwa a garuruwa daban-daban, mutane da yawa yanzu suna cike da fargaba da damuwa. Babban dalilin hakan shi ne ƙalubalen tsaro da ke ƙara tsananta a sassa daban-daban.


    Rahotanni na hare-haren ’yan bindiga, da sace-sace a kan manyan hanyoyi, da garkuwa da mutane, da rikice-rikicen da ke faruwa ba zato ba tsammani, sun sanya mutane da yawa sake tunani kafin su ɗauki hanya da sunan zuwa bukukuwan karshen shekara. Wannan yanayi ya sa wasu ke zaɓar zama a garuruwan da suke, wasu kuma suna rage nisan tafiya ko sauya tsare-tsaren bukukuwansu gaba ɗaya.


    Ko yaya bukukuwan wannan shekarar za su kasance?

    Wadanne matakai hukumomi ke dauka don kare lafiyan matafiya?

    Wadannan da ma wasu tambayoyin shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi kokarin amsawa.

    Más Menos
    15 m
Todavía no hay opiniones