Episodios

  • Yadda Sunayen Zamani Suke Neman Kawar Da Na Hausawa
    Apr 8 2026

    A tsakanin Hausawa, sunaye masu alaka da harshen Larabci sun kusan maye gurbin na gargajiya irin su Tanko da Talle da Audi da dai sauran su.

    Sai dai yayin da a da sunayen da Hausawa kan sanya wa ’ya’yansu na Annabawa ko Sahabbai ko mashahuran malaman Muslunci ne, a baya-bayan nan wasu iyaye kan aro wasu kalmomi su rika kiran ’ya’yansu da su.

    Mene ne dalilin hakan, yaushe kuma daga ina ya samo asali, kuma mene ne tasirinsa a al’adance da ma a addinance?

    Amsoshin wadannan da ma wasu tambayoyi makamantansu shirin Daga Laraba na wannan makon zai binciko

    Más Menos
    28 m
  • Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?
    Apr 1 2026

    A cikin ‘yan shekarun nan, batun garkuwa da mutane ya zama babban kalubale ga tsaro a Najeriya da wasu ƙasashen duniya.


    Lokacin da mutane suka fada hannun masu garkuwa, iyaye da ‘yan uwa sau da yawa suna fuskantar babban zabi mai wahala: biyan kudin fansa don sakin wanda aka sace ko tsayawa da kafafun tsaro har zuwa samun taimakon hukumomi.
    Shin ko ya kamata alumma su cigaba da biyan kudin fansa idan an yi garkuwa da ‘yan uwansu?


    Wannan shine batun da shirin Najriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a akai.

    Más Menos
    22 m
  • Yadda 'Yanbindiga Ke Amfani Da Hakar Zinare Wajen Mallakar Makamai
    Mar 25 2026

    Kiyasi ya nuna cewa Najeriya tana asarar sama da dala biliyan 9 a duk shekara sakamakon ayyukan masu hakar ma'adinai ba bisa ka'ida ba, kuma kaso mafi tsoka shi ne fannin zinare.

    Rahotanni sun ce hakan na karawa ‘yan ta’adda karfi, inda suke amfani da wannan dama wajen tara muggan makamai a yankin Arewa maso Yamma da ke fama da matsalar tsaro.

    'Yan bindigar sun yi ikirarin suna samun kimanin naira miliyan 300 duk mako daga haramtattun wuraren hakar ma’adinai.

    Shirin Daga Laraba na wannan makon, bincike ne kan yadda ‘yan ta’adda ke amfani da albarkarun kasa na zinare wajen siyan makamai a yankin arewa maso yamma.

    Más Menos
    28 m
  • Dalilan Tashin Farashin Kayan Miya Gabanin Bikin Sallah
    Mar 18 2026

    Yayin da sallah ya gabato, mutane da dama kan yi fadi tashi don biyan wasu bukatun su na bukukuwan sallah, kuma kamar yadda aka saba, a irin wannan lokaci ne iyalai da dama kan maida hankulan su don ganin sun biya wasu daga cikin bukatun su musamman wadanda suka jibanci bikin sallah.

    Siyayyan kayan kayan abinci na daya daga cikin wadannan hidindimu, sai dai kayan miya da suka zama dole ayi amfani dasu yayin bikin sallah sun yi tashin gwauron zabo inda alumma da dama ke ta bayyana damuwar su kan wannan batu.

    shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa farashin kayan miya suka yi tashin gwauron zabo gabanin bikin Sallah.

    Más Menos
    26 m
  • Yadda Sinadaran Dandanon Abinci Ke Yin Illa Ga Lafiya
    Mar 11 2026

    A yau, yawancin mutane suna amfani da sinadaran dandano wajen girki domin ƙara wa abinci ɗanɗano da ƙamshi. Amma, binciken masana ya nuna cewa ana yawan amfani da su fiye da yadda ake bukata, musamman irin waɗanda aka sarrafa a masana’antu.

    Wannan rashin kiyaye ƙa’ida yana iya jawo matsalolin lafiya.

    Sau da yawa mutane kan manta cewa a cikin waɗannan sinadarai akwai gishiri mai yawa da wasu ƙarin abubuwan da idan aka tara su a jiki na dogon lokaci, na iya haifar da illa.

    Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba ne kan irin matsalolin da amfani da sinadarin dafa abinci fiye da kima ke jawowa ga lafiyar mutane.

    Más Menos
    26 m
  • Takaddamar Da Ta Dabaibaye Zargin Sacewa Tare Mayar Da Walida Abdullahi Kirista
    Feb 25 2026

    Takaddama ta dabaibaye batun wata matashiya mai suna Walida Abdullahi, bayan iyalanta sun zargi wani jami’in Department of State Services mai suna Ifeanyi Onyewuenyi da sace ta daga gidansu tare da tsare ta na tsawon lokaci ba tare da sanin inda take ba.

    Rahotanni sun ce ana zargin jami’in ya sauya mata addini daga Musulunci zuwa Kiristanci tare da canza mata suna zuwa Chinaza, lamarin da iyalanta suka ce an yi ba tare da yardarta ba ko kuma amincewar danginta.


    Haka kuma, bayan shafe lokaci mai tsawo a hannunsa, an ce Walida ta haifi jaririya mace, abin da ya kara jawo cece-kuce da damuwa a tsakanin iyalanta da kuma al’umma, musamman dangane da zargin take mata ’yanci da kuma amfani da iko ba bisa ka’ida ba.

    Lamarin ya jawo kira daga kungiyoyi da masu rajin kare haƙƙin ɗan Adam da su ke bukatar gudanar da cikakken bincike domin gano gaskiya, tare da tabbatar da adalci ga Walida da kuma hukunta duk wanda aka samu da laifi idan har zarge-zargen sun tabbata.


    Shirin Daga Laraba na wannan mako ya yi duba ne kan takaddamar da ta dabaibaye batun walida Abdullahi wata da ake zargin wani jami’in hukumar DSS da sacewa.

    Más Menos
    31 m
  • Halin Da Zawarawa Ke Tsintar Kansu A Ciki A Watan Ramadan
    Feb 18 2026

    Kowane Musulmi da yadda yakan shiga watan Ramadana – wani kan shiga da shiri, wani kuma da shiririta.


    Sai dai wasu watan kan zo musu da kalubale – ba don sun shirya mishi b aba kuma don sun gaza shiryawa.
    Wani rukunin wadannan mutane shi ne na zawarawa, wadanda galibi ba su da masu agaza musu.


    Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne a kan rayuwar mata zawarawa musamman a watan Ramadana.

    Más Menos
    31 m
  • Yadda Bude Kan Iyakokin Najeriya Da Jamhuriyar Benin Da Niger Zai Amfani Alummar Kasashen
    Feb 11 2026

    A watan Agustan shekarar 2019, gwamnatin Najeriya ta rufe kan iyakokinta da wasu ƙasashe makwabta ciki har da Jamhuriyar Nijar da Jamhuriyar Benin. Wannan mataki a wancan lokaci an ɗauke shi ne domin yaƙi da fasa-kwauri, hana shigo da kaya ba bisa ƙa’ida ba, da kuma kare tattalin arziƙin cikin gida.


    Bayan wannan tsawon lokaci da aka dauka na takaita zirga-zirga tsakanin wadannan kasashe, lamarin ya shafi kasuwanci, da mu’amalar jama’a da kuma rayuwar al’ummomin da ke zaune a kan iyaka.
    Sai dai bayan wannan tsawon lokaci a kwanan nan gwamnatin Najeriya ta sanar da sake bude iyakokinta da wadannan kasashe biyu, a wani mataki na farfaɗo da kasuwanci, da ƙarfafa haɗin kai da kuma bunƙasa tattalin arziƙin yankin.


    Ko yaya bude wadannan iyakoki zai amfani kasashen biyu?
    Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

    Más Menos
    21 m